Connect with us

Interview

Hatsarin Mota Ya Yi Sanadin Raunata Mutum 22 Waɗanda Ke Tattakin Bikin Kirsimeti

Published

on

FB IMG 1735188763486
Spread the love

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Wani hatsarin mota ya yi sanadin raunata mutum 22 waɗanda ke tattakin bikin kirsimeti a Gombe, babban birnin jihar Gombe da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Lamarin ya faru ne da safiyar Laraba, yayin da mabiya addinin Kirista ke wani tattaki a cikin garin na Gombe, kamar yadda suka saba a kowace shekara.

Advertisement

Wani Jirgin Rundunar Sojin Saman Najeriya Ya Hallaka Mutane Da Dama A Sokoto 

Kakakin rundunar ƴansandan Najeriya a jihar, ASP Buhari Abdullahi ya ce “wata mota ƙirar sharon, maƙare da kayan hatsi ce ta afka cikin masu jerin gwanon ta baya, inda ta buge mutane da dama”.

“Wasu daga cikin waɗanda aka bugen sun samu raunuka har da karaya, kuma an garzaya da su zuwa asibiti domin samun kulawa.”

ASP Abdullahi ya ce jami’an tsaro sun samu nasarar ceto direban motar wanda mutane suka hau shi da duka, lamarin da ya so ya haifar da hatsaniya.

Advertisement

Duk da haka, jami’in ya ce masu tattakin sun kammala ziyarar da suka shirya yi a ranar bikin na kirsimeti.

A yau Laraba ne mabiya addinin Kirista a faɗin duniya suka yi bukukuwan Kirsimeti domin murnar zagayowar ranar da aka haifi Yesu Almasihu.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *