Connect with us

News

Bai dace a dinga ɓata sunan Fulani ba – Gwamnan Kano

Published

on

Spread the love

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce ɓatanci da ake yi wa Fulani a fadin kasar bai dace ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin tawagar kungiyar Tabital Fulaku ta reshen Kano.

Advertisement

Kwamishinan yada labarai ya kaddamar da wadanda za su rika tallata aiyukan gwamnatin Kano a Tiktok

Gwamnan, wanda ya samu wakilcin, Mataimakinsa , Aminu Abdussalam Gwarzo, ya sake tabbatar da kudirin gwamnatin jihar na mara wa kungiyar Tabital Fulaku baya wajen hada kan al’ummar Fulani a fadin kasa.

Haka kuma, ya yi kira ga shugabannin Fulani su ci gaba da jajircewa wajen bai wa matasa jagoranci mai kyau, tare da jaddada muhimmancin goyon bayansu da jagorancin su ga al’umma.

Gwarzo ya nuna damuwa kan batanci da ake yi wa Fulani a wasu kafafen yada labarai, duk da irin gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban Najeriya kamr yanda Jaridar DAILY NIGERIAN ta Ruwa

Advertisement
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *