News
Bai dace a dinga ɓata sunan Fulani ba – Gwamnan Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce ɓatanci da ake yi wa Fulani a fadin kasar bai dace ba.
Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin tawagar kungiyar Tabital Fulaku ta reshen Kano.
Kwamishinan yada labarai ya kaddamar da wadanda za su rika tallata aiyukan gwamnatin Kano a Tiktok
Gwamnan, wanda ya samu wakilcin, Mataimakinsa , Aminu Abdussalam Gwarzo, ya sake tabbatar da kudirin gwamnatin jihar na mara wa kungiyar Tabital Fulaku baya wajen hada kan al’ummar Fulani a fadin kasa.
Haka kuma, ya yi kira ga shugabannin Fulani su ci gaba da jajircewa wajen bai wa matasa jagoranci mai kyau, tare da jaddada muhimmancin goyon bayansu da jagorancin su ga al’umma.
Gwarzo ya nuna damuwa kan batanci da ake yi wa Fulani a wasu kafafen yada labarai, duk da irin gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban Najeriya kamr yanda Jaridar DAILY NIGERIAN ta Ruwa
-
News7 days ago
Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Talla Da Masu Sana’ar Jari Bola Su Bar Karkashin Gadar Tal’udu
-
News3 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
