Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Kwalejin Kimiyya Da Fasaha A Abuja Tare Da Sanya Mata Sunansa A Abuja 

Published

on

DAGA MAIMUNA RABIU UMAR 

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa Kwalejin Kimiyya ta tarayya a yankin Gwarinpa na babban birnin tarayya (FCT), wadda za ta kasance a matsayin “Kwalejin Kimiyya Ta Bola Ahmed Tinubu, Gwarinpa.” An kafa ta don tallafawa ilimin fasaha, da sana’o’i, da kuma kasuwanci a Nijeriya.

Advertisement

A cikin wata wasiƙa da Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya aika wa Ministan FCT, Nyesom Wike, a ranar 16 ga Janairu, 2025, ya nemi a ware wurare da suka dace don kafa rukunin wucin gadi da na dindindin na makarantar. Kwamitin fasaha daga ma’aikatar ilimi da hukumar NBTE za su duba wuraren kafin ba da izinin ƙarshe.

Tankar Mai Ta Kuma Faduwa A  Niger Inda  Mutane Sunje Ɗiban Ganima.

Shugaban ƙaramar hukumar AMAC, Christopher Zakka Maikalangu, ya yabawa shugaban ƙasa bisa wannan matakin, yana mai cewa kafa makarantar zai ƙara wa mazauna FCT ci gaba da ilimi mai amfani.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending