Connect with us

News

Hisbah ta kama masoya da su ka ɗaura auren su a gidan cin abinci a Kano 

Published

on

Hukumar Hisbah Haramta Zancen Dare A Mota A Kano

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta cafke wani mutum da budurwar sa bisa daura aurensu a gidan cin abinci na Banana da ke titin gidan zoo a Kano.

Advertisement

Mataimakin babban kwamandan hukumar, Dakta Mujahideen Abubakar, ya tabbatar da kamen ga jaridar PUNCH Online a yau Alhamis, inda ya bayyana cewa jami’an Hisbah sun kai farmaki gidan abincin ne a daren jiya Larabar, biyo bayan samun bayanan sirri.

Godiya Ga Kungiyar Gwamnonin Najeriya Da Suka Yi Gyaran Fuska Ga Kudirin Gyaran Haraji —Dokta Lajada

“Abin takaici ne a gaya muku cewa abokan mutumin ne suka gudanar da daurin auren a gidan abinci ba tare da amincewar iyayen ma’auratan ba,” in ji shi.

Advertisement

Ya yi gargadin cewa hukumar ba za ta nade hannunta ta barin wasu abubuwan da ba a so su ci gaba da keta shari’a a jihar Kano ba

A cewarsa, tun daga lokacin ne hukumar ta kaddamar da farautar dukkan baki da suka halarci haramtaccen daurin auren.

Advertisement

“Mun kama ma’auratan. Muna bin abokan angon da suka gudu daga gidan abincin bayan da jami’an mu suka afkawa wurin,” ya kara da cewa.

Mataimakin kwamandan ya ce ma’auratan sun saba wa dukkanin sharuddan daurin aure, wanda hakan ya saba wa Shari’a.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending