Connect with us

News

Jami’an Hisbah Sun Kama Wadanda Suka Shirya Taron Casu Na Bankwana Da Shaidan A Kano 

Published

on

Hukumar Hisbah Haramta Zancen Dare A Mota A Kano

Hukumar Hisbah a Jihar Kano ta kama mata shida da maza uku bisa zargin shirya taron casu da suka kira na bankwana da Shaidan yayin da ake shirin shiga watan Azumin Ramadana a wani shiri da suka gudanar mai taken Operation Ramadan Karim.

Mataimakin Babban Kwamandan Hisbah a Jihar Kano, Dakta Mujahid Aminuddeen, ne ya bayyana hakan.

‎Little Ya Jajantawa Yan Kasuwar Singa Bisa Ibtila’in Gobara

Ya ce matasan sun shirya taron casu tare da gayyatar wasu fitsararrun mawaƙa masu yaɗa baɗala domin raƙashewa da sunan suna bankwana da Shaiɗan, lamarin da ya sabawa ka’idojin tarbiyya da doka a jihar Kano.

Ya kara da cewa da zarar an kammala bincike a kansu za a gurfanar da su a gaban Kotu.

Ya kuma bukaci al’umma su ci gaba da sa ido tare da bai wa hukumar rahoton duk wani abu da suka gani da ya saba wa tarbiyya ko doka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending