Connect with us

News

Dattijo Mai Shekaru 50 Ya Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga, Sun Yi Garkuwa Da Ɗansa Da Iyalansa

Published

on

Dattijo Mai Shekaru 50 Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga Domin Yin Garkuwa Da Ɗansa Da Iyalansa

DAGA NUSIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

An kama wani dattijo mai shekaru 50, Ado Haruna, bisa laifin ba da bayanan sirri ga ‘yan bindiga, inda suka yi garkuwa da ɗan yayarsa, Alhaji Bashiru Anas, tare da iyalansa a Zariya, Jihar Kaduna.

Advertisement

Duk da cewa an biya har Naira miliyan 13 a matsayin kudin fansa, tare da sabbin babura hudu da katin kiran waya na Airtel na Naira 300,000, Haruna ya samu Naira 200,000 kacal daga rabon kudin.

Ribadu Ya Nemi Naja’atu Ta Janye Kalaman Zargi Kansa Ko Su Wanye A Kotu

Jami’an rundunar lalubo bayanan sirri sun cafke Haruna, wanda aka bayyana a Abuja a matsayin daya daga cikin mutanen da ke da hannu a manyan laifuka.

Advertisement

Haruna, mazaunin Unguwar Kanawa Dutse Abba, ya jagoranci wasu ‘yan bindiga uku zuwa gidan Alhaji Anas da tsakar dare, inda suka yi awon gaba da matansa biyu, ‘ya’yansa uku, kaninsa, da matar kaninsa bayan sun tarar da shi ba ya nan.

An tsare iyalin har tsawon kwanaki 60 a dazukan Buruku da Sabo Birni. A lokacin da yake tabbatar da rawar da ya taka, Dattijo mai shekaru 50 ya amsa cewa ya nuna wa ‘yan bindiga gidan Alhaji Anas, wanda ya kira da “dan yayata.”

Advertisement

Wannan kame na kara tabbatar da yadda wasu ke hadin baki da ‘yan ta’adda don cutar da na kusa da su, duk da irin radadin da hakan ke haifarwa ga iyalai da al’umma baki ɗaya.

 

Advertisement

 

DAILY TRUST 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending