Connect with us

News

An Kama Mutane 17 A Kano Bisa Zargin Shiryawa Tayar Da Tarzoma

Published

on

download (1)

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da kama matasa 17 da ake zargi da shirya tayar da zaune-tsaye a wasu sassan jihar, wanda ya kai ga rufewar. titin zuwa gidan Gwamnatin Jihar Kano.

Rahotanni na nuni da cewa rundunar, tare da hadin gwiwar sauran hukumomin tsaro, ta tura jami’anta domin tabbatar da doka da oda a yayin da ake samun rahotanni game da zanga-zangar da wasu ke shiryawa.

Burinmu shi ne Barau FC ta sami gurbin shiga gasar zakarun Nahiyar Africa (CAF Confederation) – DSP Barau

A cikin sanarwa da Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, ya bayyana cewa an kama mutanen da ake zargi kuma bincike kan lamarin ya fara.

Rundunar ta tabbatar da cewa za a ci gaba da samar da tsaro don kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da kira ga jama’a da su baiwa hukumomi rahoton duk wani motsi da bai dace ba.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending