Connect with us

News

Ma’aikatan Hukumar Samar Da Ruwan Sha Sun Janye Yajin Aiki A Kano

Published

on

Ma'aikatan Hukumar Ruwan Sha Sun Janye Yajin Aiki a Kano

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Ma’aikatan hukumar samar da ruwan sha ta jihar Kano sun janye yajin aikin da suka shiga tun ranar 26 ga watan Fabrairun 2025, sakamakon rashin sanya su a sabon tsarin mafi karancin albashi na gwamnati.

Advertisement

Shugaban kungiyar kwadago ta hukumar, Kwamared Najib Abdulsalam, ya tabbatar da janye yajin aikin yayin tattaunawa da tashar Dala FM a daren jiya.

Ya bayyana cewa janye yajin aikin ya biyo bayan zaman tattaunawa da suka yi da bangarorin gwamnati da lamarin ya shafa.

Advertisement

Martanin ‘Yan Mazaɓar Tarauni Ga Yarima: “Mu Ba Dawakai Ba Ne Da Za Ka Ba Mu Dawa”

“Daga cikin wadanda muka gana da su akwai Kwamishinan Kasafi da Tsare-Tsare na Kano, shugaban NLC na jihar, da wasu manyan sakatarorin gwamnati da kuma masu ba gwamna shawara,” in ji Kwamared Najib.

Ya kuma umarci dukkan ma’aikatan hukumar da su koma bakin aiki daga gobe, Talata 04 ga watan Maris 2025.

Advertisement

Tun farko dai ma’aikatan sun tsunduma yajin aiki ne bisa rashin fara biyan su sabon mafi karancin albashi, wanda gwamnatin Kano ta ki aiwatarwa tsawon watanni hudu.

Hakan na nufin cewa da janye yajin aikin, ana sa ran sake samun wadataccen ruwan sha a Kano bayan makwannina tsaiko.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending