News
Najeriya Ta Matsa Zuwa Matsayi Na Shida A Ƙididdigar Ta’addanci A Duniya Inda A 2024 Aka Kashe Mutane 565
Wani rahoton ƙididdigar ta’addanci na duniya ya bayyana cewa Najeriya ta matsa zuwa matsayi na shida a jerin ƙasashen da suka fi fuskantar ta’addanci a duniya, daga matsayi na takwas da take a shekarun 2023 da 2024.
Rahoton wanda aka fitar ranar 5 ga watan Maris, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, ya nuna cewa mutane 565 ne suka rasa rayukansu sanadiyyar ta’addanci a Najeriya a shekarar 2024.
Abia, Kano da Ebonyi Sune Kan Gaba Wajen Yawan Yaran da Ba Sa Kammala Babbar Sakandare – Rahoto
A cewar rahoton, Burkina Faso ce ke kan gaba a matsayin ƙasa mafi fama da ta’addanci, sai Pakistan da Syria a matsayi na biyu da na uku. Kasashen Mali da Jamhuriyar Nijar ne ke biye, yayin da Najeriya ke matsayi na shida.
Sauran ƙasashen da ke cikin jerin ƙasashen 13 da suka fi fama da ta’addanci sun haɗa da Somalia, Kamaru da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo.
Rahoton ya nuna cewa yawaitar hare-haren ‘yan ta’adda da rashin tsaro na ci gaba da ƙara sanya ƙasashen Afirka cikin jerin ƙasashen da ta’addanci ya fi kamaria duniya.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
