News
Gobara Ta Lakume Rayuka 7, Ta Haddasa Asarar Naira Miliyan 50 A Kano
Aƙalla mutum bakwai ne suka rasa rayukansu, yayin da gobara ta haddasa asarar kadarori na sama da Naira miliyan 50 a Jihar Kano a watan Fabrairun 2025.
Kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusif Abdullahi, ya bayyana cewa hukumar ta samu jimillar kiraye-kirayen kashe gobara guda 77, kiraye-kirayen neman ceto 11, da kuma ƙaryar kiran gobara guda uku a cikin watan.
Dalilin Da Ya Sanya Rundunar ‘Yan Sandan Kano Karrama Wakilin Muhasa TV & Radio
Ya ƙara da cewa, an kiyasta darajar kadarorin da gobarar ta lalata a cikin watan Fabrairu da N50,318,000, yayin da jami’an kashe gobara suka ceto kadarori da darajarsu ta kai N180,318,000.
Hukumar ta yi kira ga jama’a da su yi taka-tsantsan wajen amfani da wuta domin gujewa afkuwar gobara, tare da shawarci direbobi da su tuka mota cikin kulawa da bin dokokin hanya don guje wa haɗurra.
