News
Wani Hatsarin Mota Ya Sake Faruwa A Gadar Karu A Abuja, Kwana Daya Bayan Mutuwar Mutum 10
Wani sabon hatsarin mota ya sake faruwa a kusa da gadar Karu, kan titin Abuja-Keffi Expressway, sa’o’i 24 bayan hadarin babbar mota dauke da iskar CNG da ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutum 10.
A cewar rahotanni, wannan sabon hatsarin ya afku ne da misalin karfe 3:54 na yammacin Alhamis, inda babbar mota dauke da takin zamani ta yi karo da wata mota kirar Hijet da kuma wata babbar mota dauke da yashi (tipper).
Sai dai, a cewar shugaban sashen hulda da jama’a na hukumar bada agajin gaggawa ta Abuja (FCT Emergency Management Department), Nkechi Isa, babu asarar rai a wannan hatsarin.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, Isa ta bukaci direbobi da su rika taka-tsantsan yayin tuki, tare da bayyana cewa jami’an hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) suna aiki don kawar da ragowar motoci a wurin domin hana cunkoso.
