Connect with us

News

An Rushe Gine-Gine A Badalar ‘Dan Agundi A Kano

Published

on

IMG 20250326 WA0017

A daren jiya, wasu gine-gine guda biyu da ke yankin Badalar ‘Dan Agundi, Kano, sun fuskanci rusau da ba a bayyana masu alhaki ba. Shaidu sun ce jami’an tsaro dauke da bindigu sun kama mai gadin wajen tare da sanya masa ankwa kafin fara aikin rusau.

Advertisements
Advertisements

AREWA RADIO ta ruwaito cewa filayen da aka rushe na daga cikin wuraren da ake takaddama a kotu tsakanin masu ginin da Hukumar Tsara Birane ta Jihar Kano.

Advertisements

Gwamnatin Kano Ta Neman Hadin Gwiwa Da Saudiyya Wajen Gina Cibiyar Maganin Zuciya da Fitsari

Tun farkon mulkinsa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna shirin rushe gine-ginen da aka yi a yankunan Badalar ‘Dan Agundi zuwa Kofar Fanfo, inda aka ce tsohuwar gwamnatin Kano ce ta raba filayen.

Advertisements
Advertisements

Har yanzu babu wata hukuma da ta fito fili ta dauki alhakin rushewar, amma al’umma sun nuna damuwa kan yadda aka gudanar da aikin a cikin dare, lamarin da ke kara dagula rikicin mallakar wuraren.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending