News
Majalisar Wakilai Za Ta Haramtawa Masu Shekaru Sama da 60 Tsayawa Takara
Majalisar Wakilan Najeriya ta tsallake karatu na biyu kan kudurin dokar da ke neman hana ‘yan takarar shugaban kasa da gwamna masu shekaru sama da 60 shiga takara.
A zaman majalisar na yau Alhamis, an amince da kudurin bayan gabatarwar dan majalisa, Hon. Ikeagwuonu Ugochinyere, wanda ke neman a yi garambawul ga wasu sassa na kundin tsarin mulkin kasa na 1999.
Titin Jirgin Ƙasa Daga Legas Zuwa Kano Zai Fara Aiki —Hukumar NRC
Rahotanni sun bayyana cewa idan kudurin ya tsallake karatu na uku, kuma shugaban kasa ya sanya hannu a kai, zai canza tsarin cancantar tsayawa takara a kasar.
Daga cikin muhimman sauye-sauyen da kudurin ya kunsa sun hada da:
Duk wanda ya haura shekaru 60 ba zai iya tsayawa takarar shugaban kasa ko gwamna ba.
Dole ne duk wani dan takara ya mallaki digiri na farko a bangaren da ya fi kwarewa, a matsayin mafi karancin matakin ilimi.
Kudurin ya bukaci a yi gyara a sashe na 131 na kundin tsarin mulkin kasa don iyakance shekarun takarar shugaban kasa, da sashe na 177 don gwamnonin jihohi.
Baya ga wannan kuduri, majalisar ta kuma amince da wasu kudurori daban-daban da suka shafi cigaban Najeriya.
Sai dai Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Jam’iyyun PDP, CUPP da SDP Sun Yi Allah wadai da matakin da Majalisar Wakilan Najeriya ta dauka na kakaba iyakar shekaru ga masu neman mukaman shugaban kasa da gwamna a kasar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
