Connect with us

News

Majalisar Shari’ar Musulunci Ta Naɗa Sheikh Bashir Aliyu Umar A Matsayin Sabon Shugaba

Published

on

c1tm1jqgI5THVz9xNxNsYFGqjXKT9z8m5JhTYEB0

Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya (NSCJ) ta sanar da naɗin Sheikh Dr. Bashir Aliyu Umar a matsayin sabon shugaban majalisar, biyo bayan rasuwar tsohon shugaban majalisar, Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.

Sanarwar da sakataren majalisar, Malam Nafiu Baba Ahmed, ya fitar a yau Laraba, ta bayyana cewa Sheikh Bashir, wanda ke rike da mukamin mataimakin shugaba a baya, ya hau kujerar shugabanci kai tsaye bisa tsarin da ke akwai.

Advertisement

Gwamnatin Kano Ta Ware Sama da Naira Biliyan 15 Don Biyan Tsofaffin Kansilolin Zamanin Ganduje

Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah ya rasu ne a ranar Litinin da ta gabata yana da shekara 81 a jihar Osun, inda ya kwashe shekaru da dama yana jagorantar harkokin majalisar da kuma ba da gudummawa wajen ci gaban shari’ar Musulunci a Najeriya.

Majalisar ta kara da cewa za a sanar da sabon mataimakin shugaban majalisar a wani lokaci mai zuwa.

Advertisement

Sheikh Dr. Bashir Aliyu Umar, wanda aka nada shugaban majalisar, sanannen malami ne a fagen ilimin addini da kuma limamin masallacin Juma’a na Al-Furqan da ke jihar Kano. Ya shahara da ilimi mai zurfi da kuma kishin addinin Musulunci.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending