Connect with us

News

‎Yadda Ƴan Najeriya Za Su Nemi Aikin NSCDC, NIS, NCoS Da FFS

Published

on

images

Gwamnatin tarayya ta sanar da ɗaukar ma’aikata 30,000 a hukumomin Immigration, Civil Defence, Correctional da Fire Service a faɗin ƙasar.

‎Kwamitin CDCFIB ya ce ɗaukar aikin zai haɗa da guraben aiki a Hukumar Kula da Shige da Fice, Hukumar Gidajen Gyaran Hali, Hukumar Kashe Gobara da NSCDC.

Advertisement

Taron Jin Ra’ayin Jama’a Kan Sauya Kundin Tsarin Mulki: Sanata Barau Na Jagorantar Yunkurin Kawo Sauyi

‎Za a buɗe ƙofar neman aiki ranar 26 ga Yuni a shafin: recruitment.cdcfib.org.

‎Masu nema dole ne su zama ‘yan Najeriya masu shekaru 18 zuwa 35 da cika ƙa’idojin lafiyar jiki da ta hankali.

Advertisement

‎Maza su kai tsayin 1.65m da faɗin ƙirji 0.87m; mata kuwa su kai aƙalla 1.60m.

‎Dole ne masu nema su zama masu kyakkyawan hali, ba tare da tarihin laifi ba.

Advertisement

‎Ana buƙatar takardar kammala sakandare tare da nasarar cin aƙalla darussa huɗu ko biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi.

‎Masu NCE, OND, HND, digiri ko takardun sana’a a fannonin fasaha suma ana ƙarfafa musu gwiwa su nema, The Cable ta ruwaito.

Advertisement

‎An gargaɗi masu nema da su tsaya a hukuma guda ɗaya kawai, domin neman gurabe fiye da ɗaya zai janyo ƙin amincewa.

‎Ana sa ran rufewar shafin neman aikin cikin makonni uku bayan buɗe ƙofar neman aikin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending