News
Prof. Gwarzo Ya Bai Wa Cibiyar Koyar Da Harshen Faransanci Ta Alliance Francaise Ofishi A Kano
Shugaban rukunin Jami’o’in MAAUN, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, ya bai wa cibiyar koyar da harshen Faransanci ta Alliance Francaise da ke Kano gini mai hawa biyu domin zama ofishinta na dindindin.
Prof. Gwarzo ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis, inda ya bayyana cewa ginin da ke kan titin Filin Jirgin Sama, kusa da unguwar Ahmadiyya a Kano, yanzu ya koma mallakin Alliance Francaise.
“Mun cimma matsaya da Gwamna Fubara, mun yanke shawarar aiki tare” —Wike
Ya ce wannan mataki na daga cikin kokarinsa na tallafa wa ci gaban koyon harshen Faransanci a Kano, musamman ganin irin rawar da cibiyar ke takawa wajen bunkasa ilimin yare da al’adu tsakanin Najeriya da Faransa.
“Alliance Francaise ta shafe fiye da shekaru 30 tana aiki a Kano ba tare da mallakar ofishi na dindindin ba. Wannan ne ya sa na yanke shawarar bayar da wannan gini domin taimakawa su samu wuri na dindindin,” inji shi.
Prof. Gwarzo ya ce an tanadi dukkan kayan more rayuwa da ake bukata a cikin ginin, ciki har da kayan daki da kuma tsarin samar da wutar lantarki ta hasken rana domin tabbatar da ingantaccen aiki.
Ya bayyana cewa wannan tallafi nasa wani mataki ne na yin koyi da babban dan kasuwa daga Legas, Mike Adenuga, wanda ya taba bayar da gini ga Alliance Francaise a Legas.
Farfesan ya ce yana da yakinin cewa wannan gudummawa za ta taimaka matuka wajen habaka koyar da harshen Faransanci a Kano da ma Najeriya baki daya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
