Connect with us

News

Ambaliya Ta Lalata Gidaje Fiye Da 100 A Zakirai

Published

on

Fiye da gidaje 100 ne suka lalace sakamakon ambaliya a garin Zakirai, da ke ƙaramar hukumar Gabasawa a jihar Kano, bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka tafka a yankin.

Advertisements
Advertisements

Ambaliyar ta kuma shafi wani ɓangare na layin dogo da kuma kasuwar garin, inda mazauna suka dora alhakin hakan a kan aikin  titin kilomita biyar da ke gudana a yankin, wanda suka ce ba a samar da ingantattun magudanan ruwa ba.

Advertisements

‎Al’ummar Kofar Kaza A Kano Sun Gudanar Da Sallar Qunut Kan Zargin Wani Hakimi Da Mamaye Filayensu

“Ruwan yana shigowa cikin gidajenmu kai tsaye. Wasu daga cikinmu sun bar gidajensu, wasu kuma na zaune a cikin ruwa. Abincin da muka tanada ya lalace. Muna roƙon agajin gaggawa daga gwamnati da masu hannu da shuni,” in ji Sa’adatu, wata mazauniyar unguwar.

Advertisements
Advertisements

Masana da mazauna yankin sun ce Zakirai ba ta da tarihin ambaliya, sai bayan fara aikin titin .

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending