News
Sarkin Katsinan Gusau, Dakta Ibrahim Bello ya rasu
Sarkin Gusau Alhaji Dakta Ibrahim Bello wanda aka fi sani da Sarkin Katsinan Gusau ya rasu.
Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya FRCN ne ya tabbatar da rasuwar a safiyar Juma’a.
INEC: An Karɓi Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu 144 A Fadin Ƙasa
Ya rasu yana da shekara 71 a wani asibiti da ke Abuja babban birnin Nijeriya.
An naɗa Dakta Ibrahim Bello Sarkin Gusau na 15 a ranar 16 ga watan Maris ɗin 2015, a zamanin gwamnan Abdulaziz Yari.
Ya gaji ɗan uwansa Alhaji Muhammad Kabiru Danbaba wanda ya rasu a wani asibiti a Abuja a ranar 5 ga Maris ɗin 2015, kamar yadda gidan rediyon FRCN ya tabbatar.
-
News23 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News2 days ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
