News
Gwamnatin Kano Za Ta Maida Gidan Yarin Kurmawa Cibiyar Tarihi Da Raya Al’adu
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana kudirinta na sauya fasalin gidan gyaran hali na Kurmawa da ke tsakiyar birnin Kano, inda za ta mayar da shi cibiyar adana tarihi da raya al’adun gargajiya na jihar.
Sanarwar hakan na kunshe ne a wani sako da Babban Mai Taimaka wa Gwamna Abba Kabir Yusuf kan kafafen sada zumunta, Salisu Yahaya Hotoro, ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar.
A cewarsa, gwamnati za ta kwashe dukkanin fursunonin da ke Kurmawa zuwa sabon gidan yari na Janguza, tare da mayar da tsohon ginin Kurmawa cibiyar yawon buɗe ido da ke kunshe da kayan tarihi da fasahar gargajiya.
Shi ma mai ba Gwamnan Kano shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Ibrahim Adam, ya tabbatar da wannan mataki da gwamnatin ke shirin dauka, yana mai cewa:
“Gwamnatin jihar Kano zata kwashe dukkanin daurarrun dake gidan gyaran hali na Kurmawa a mayar da su Janguza, sannan za’a mayar da gidan gyaran hali na Kurmawa din ya koma gidan adana kayayyakin tarihi da raya al’adu na jihar Kano.”
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
