Connect with us

News

Gwamnatin Kano Za Ta Maida Gidan Yarin Kurmawa Cibiyar Tarihi Da Raya Al’adu

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana kudirinta na sauya fasalin gidan gyaran hali na Kurmawa da ke tsakiyar birnin Kano, inda za ta mayar da shi cibiyar adana tarihi da raya al’adun gargajiya na jihar.

Sanarwar hakan na kunshe ne a wani sako da Babban Mai Taimaka wa Gwamna Abba Kabir Yusuf kan kafafen sada zumunta, Salisu Yahaya Hotoro, ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar.

‘Yan bindiga sun sace fiye da mutum 50 a Jihar Zamfara

A cewarsa, gwamnati za ta kwashe dukkanin fursunonin da ke Kurmawa zuwa sabon gidan yari na Janguza, tare da mayar da tsohon ginin Kurmawa cibiyar yawon buɗe ido da ke kunshe da kayan tarihi da fasahar gargajiya.

Shi ma mai ba Gwamnan Kano shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Ibrahim Adam, ya tabbatar da wannan mataki da gwamnatin ke shirin dauka, yana mai cewa:

“Gwamnatin jihar Kano zata kwashe dukkanin daurarrun dake gidan gyaran hali na Kurmawa a mayar da su Janguza, sannan za’a mayar da gidan gyaran hali na Kurmawa din ya koma gidan adana kayayyakin tarihi da raya al’adu na jihar Kano.”

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending