Connect with us

News

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Muhimmancin Bin Ka’ida A Aikin Jarida

Published

on

IMG 20250821 WA0002

Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta ci gaba da yin aiki tare da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da bin ƙa’ida da ɗabi’a a aikin jarida.

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana haka ne lokacin da ƙungiyar Young Female Professionals in Media (YFPM) ta kai masa ziyara a ofishinsa.

Advertisement

China Ta Ƙera Saƙago Da Zai Iya Ɗaukar Cikin Haihuwa 

Ya ce gwamnatin Kano ta damu da yadda ake yawaita bayanai marasa inganci a kafafen sada zumunta da ma kafafen gargajiya, lamarin da ya ce na iya lalata martabar jihar da kuma aikin jarida gaba ɗaya.

Kwamishinan ya kuma bayyana shirin gwamnati na haɗin gwiwa da ƙungiyar NUJ wajen kafa kwamiti na gogaggun ’yan jarida domin ƙarfafa bin ƙa’ida da inganta aikin jarida.

Advertisement

Tun da farko, Sakatariyar YFPM, Maryam Usman Nagado, ta ce ƙungiyar ta haɗu ne domin ƙarfafa mata a harkar jarida ta hanyar horo, wayar da kai da kuma samar da haɗin kai da hukumomi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending