News
Gwamna Ya Kara Albashi Zuwa N104000, Likitoci Za Su Fara Karbar N582000
Gwamnan Jihar Imo, Sanata Hope Uzodimma, ya sanar da karin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan gwamnati a jihar zuwa Naira 104,000.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a wani taro da ya gudanar tare da mambobin ƙungiyar kwadago na jihar a fadar gwamnati da ke Owerri.
‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Miji, Mata Da Kuma ‘Yarsu A Katsina
Haka kuma, an ƙara albashin likitoci a cikin ma’aikatan gwamnati na jihar zuwa Naira 582,000 a kowane wata.
Gwamna Uzodimma ya bayyana cewa wannan ƙarin albashi ya samu ne sakamakon ƙarin kudaden da jihar ke samu daga cikin gida da kuma ƙarin rabon da ake samu daga gwamnatin tarayya.
Ya jaddada cewa sabon tsarin albashin zai taimaka wajen farfaɗo da tattalin arzikin jihar da kuma ƙara kwarin gwiwa da aiki tukuru a tsakanin ma’aikata.
Bugu da ƙari, Gwamnan ya sanar da ware Naira biliyan goma sha shida (N16bn) domin biyan bashin kuɗin fansho na tsofaffin ma’aikata a jihar.
-
News22 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News2 days ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
