News
Gwamnan Katsina Ya Soke Lasisin Makarantun Masu Zaman Kansu A Fadin Jihar
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Umar Dikko Radda, ya sanar da soke lasisin gudanar da harkokin dukkan makarantun masu zaman kansu da na al’umma a fadin jihar, a wani mataki na sauya fasalin tsarin ilimi.
Sanarwar ta fito ne daga Kwamishiniyar Ilimin Firamare da Sakandare, Hajiya Zainab Musa-Musawa, ta hannun mai magana da yawun ma’aikatar, Sani Danjuma, ranar Asabar a Katsina.
Dokar ta-ɓaci: Fubara zai dawo ofis ranar 18 ga Satumba — Nyesom Wike
A cewar Musa-Musawa, majalisar zartarwa ta jihar ta amince da wannan mataki a matsayin wani bangare na sabbin gyare-gyare a fannin ilimi, domin tabbatar da inganci, daidaito da kuma tsari mai nagarta na koyo da koyarwa a jihar.
Kwamishiniyar ta bayyana cewa wannan sabuwar doka ta yi daidai da manufar gwamnatin jihar kan makarantun kuɗi da na al’umma, wacce aka gabatar wa masu ruwa da tsaki a taron wayar da kai da aka gudanar a ranar 2 ga Yuni, 2025.
“Mun kuduri aniyar karfafa sa-ido da gaskiya a fannin ilimi. Wannan mataki na daga cikin hanyoyin kare makomar ‘ya’yan Katsina ta hanyar tabbatar da tsarin karatu da ya dace da ƙa’idojin duniya,” in ji Musa-Musawa.
