Connect with us

News

Sama Da Mutum Miliyan 3.5 Ne Suka Yi Rijistar Katin Zaɓe Ta Yanar Gizo – INEC

Published

on

INEC Yakubu

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce sama da ‘yan Najeriya miliyan uku da dubu dari biyar (3.5m) ne suka yi rijistar katin zaɓe ta yanar gizo cikin makonni uku kacal da fara aikin.

A sanarwar da kwamishinan INEC na ƙasa kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, Sam Olumeku, ya fitar ranar Litinin, ya ce jimillar 3,544,850 ne suka kammala rajista daga ranar 18 ga watan Agusta zuwa 7 ga Satumba.

Advertisement

GADAR ƘAUYEN KUREKEN SANI TA RUSHE: Dubban Mutane Sun Makale, Al’umma Na Roƙon Matakin Gaggawa Daga Gwamna Yusuf

Sanarwar ta nuna cewa daga cikin waɗanda suka yi rajistar, 1,709,933 (48.24%) maza ne, yayin da 1,834,917 (51.76%) mata ne.

Mafi yawan masu rijistar kuwa matasa ne ‘yan shekaru 18 zuwa 34, waɗanda suka kai 2,291,809 (64.65%). Haka kuma, 882,441 (24.89%) daga cikinsu dalibai ne.

Advertisement

INEC ta bayyana cewa nan gaba za ta wallafa cikakkun alkaluma kan waɗanda suka yi rijistar ta yanar gizo da kuma waɗanda suka je cibiyoyin rajista.

Hukumar ta kuma yaba da irin goyon bayan da ƙungiyoyi da al’umma suka bayar wajen wayar da kai, sai dai ta sake jaddada cewa ‘yan Najeriya masu shekaru 18 zuwa sama ne kaɗai suka cancanci yin rijistar katin zaɓe.

Advertisement

 

 

Advertisement

PEOPLES GAZETTE

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending