News
INEC Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban Jam’iyyar ADC
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) ta tabbatar da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata David Mark, a matsayin sabon shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), bayan wani dogon lokaci na rikici da gyare-gyare a cikin jam’iyyar.
A cikin jerin sabbin shugabannin da hukumar ta amince da su, akwai tsohon gwamnan Osun, Rauf Aregbesola, wanda aka nada a matsayin sakataren kasa.
An Gurfanar Da Mutum Biyu A Kotu Bisa Zargin Satar Waya Ta Naira Miliyan 1.9
Sauran sun hada da Dr. Ibrahim Mani a matsayin mai kula da kudi, Akibu Dalhatu a matsayin sakataren kudi, da kuma tsohon gwamnan Edo, Farfesa Oserheimen Osunbor, wanda zai rike mukamin lauya mai ba da shawara ga jam’iyyar.
A cewar INEC, wannan tantancewar za ta ba wa jam’iyyar damar hada kan mambobinta tare da gudanar da shirye-shirye na wayar da kan jama’a a fadin kasar, yayin da ADC ke kokarin karfafa matsayinta gabanin babban zaben 2027.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
