News
Gwamnatin Kano Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Ranar Hutu
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana gobe Juma’a, 19 ga Rabi’ul Awwal 1447H, wanda ya yi daidai da 12 ga Satumba, 2025, a matsayin ranar hutu domin gudanar da bukukuwan ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW).
Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Kwamared Ibrahim Abdullahi Wayya, ne ya fitar da sanarwar a madadin gwamnatin Kano.
Sanarwar ta ce hutun zai ba wa jama’a damar gudanar da bukin Takutaha, wanda ke nuni da cika kwanaki bakwai da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW).
Haka kuma gwamnatin ta yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan dama wajen nazari da kuma koyi da kyawawan halayen Manzon Allah (SAW), tare da addu’ar samun zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaban Kano da Najeriya baki ɗaya.
Gwamnatin ta kuma taya Musulmi murnar wannan gagarumin biki na Mauludi, tana mai fatan ya kasance alheri ga kowa da kowa.
