News
NDLEA Ta Cafke ’Yan Najeriya Biyu Da Suka Dawo Daga Brazil Da Hodar Iblis Da Koken
Jami’an Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) sun cafke wasu ’yan Najeriya biyu da suka dawo daga Brazil dauke da hodar iblis da koken a filin jirgin saman Murtala Muhammad da ke Ikeja, Legas.
A wata sanarwa da Daraktan yada labarai na hukumar, Femi Babafemi, ya fitar, an bayyana cewa jami’an NDLEA sun gano kwayoyin ne bayan gwajin hoton jiki da aka yi wa wadanda ake zargi, wanda ya tabbatar da cewa sun hadiye miyagun kwayoyi.
Da na so wa’adi na uku, na san yadda zan bi wajen cimma burina –Olusegun Obasanjo
Mutumin farko, Ofoma Sunday, mai shekaru 46, an kama shi ne a ranar 16 ga Satumba bayan ya iso daga Brazil ta jirgin Ethiopian Airlines. Daga bisani ya fitar da rukunai 111 na hodar iblis masu nauyin kilo 1.452 a wani otal da ya nufa domin mika kayan.
Rahoton ya ce daga nan ne aka kama Nweke Jude Chuckwudi, wanda aka tura domin karɓar kwayoyin.
Haka kuma, jami’an NDLEA sun cafke wani mutum mai suna Ukachukwu Frank Ikechukwu a ranar 19 ga Satumba bayan dawowarsa daga Brazil ta hanyar Addis Ababa. Gwajin jiki ya nuna cewa ya hadiye miyagun kwayoyi.
Daga baya ya fitar da rukunai biyar na koken masu nauyin gram 145. Ya shaida cewa a Brazil ya sayi rukunai tara ya boye a duburarsa, amma saboda radadi ya zubar da biyu a Addis Ababa, sannan ya rasa wasu biyu a cikin jirgi.
Ukachukwu ya kuma bayyana cewa tun daga 2017 yana kasuwanci a Brazil, sai dai a shekarar 2020 ya tafi Amurka inda aka kama shi da laifin shige da fice. An tsare shi sama da shekara guda kafin a kora shi zuwa Najeriya a 2022.
Shugaban NDLEA, Manjo Janar Mohammed Buba Marwa (rtd), ya yaba da jarumtakar jami’an da suka gudanar da samamen, tare da bukatar su ci gaba da jajircewa wajen dakile safarar miyagun kwayoyi a fadin kasar.
