News
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum Bisa Zargin Dukan Yaro Har Lahira Saboda Satar Koko
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Ondo ta tabbatar da kama wani mutum da ake zargi da dukan wani yaro har lahira a ƙauyen Akungba-Akoko, karamar hukumar Akoko South West, saboda zargin satar koko daga gona.
Kwamandan hulda da jama’a na rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce lamarin ya faru ne ranar Asabar, 20 ga Satumba, 2025, da misalin ƙarfe 2:30 na rana.
Jami’an KAROTA Sun Kama Kayan Da Aka Sace A Makarantar Gwamnati Na Fiye Da Naira Miliyan 80
“An kawo rahoton cewa an doke yaron sosai bayan an zarge shi da satar koko daga gona. An kai shi asibiti don samun kulawar gaggawa, amma abin takaici, yaron ya rasu a can,” in ji Ayanlade.
Ya ce an kama wanda ake zargi nan take, yayin da gawar yaron aka kai sashen mutuware domin gudanar da bincike.
A yanzu haka, lamarin yana hannun Sashen Bincike na Laifuka na Jihar (SCID), Akure, domin gudanar da bincike mai zurfi da tabbatar da adalci.
