Connect with us

News

Gwamna Kano Ya Miƙa Korafe-korafen Kungiyoyin Addini Kan Malam Lawan Triumph Zuwa Ga Majalisar Shura

Published

on

Triumph
Malam Lawan Triumph

Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya karɓi korafe-korafen da wasu kungiyoyin addinin Musulunci suka gabatar dangane da karatun da Malam Lawan Triumph ya gudanar. Gwamnan ya mika korafe-korafen zuwa Majalisar Shura ta Jihar domin yin nazari da daukar mataki.

A cikin wata sanarwa, Sakataren Yada Labarai na Gwamnatin Jihar Kano, Musa Tanko, ya bayyana cewa an samu korafe-korafen daga kungiyoyi da dama, ciki har da:

Advertisement

Tsoffin Ƴan Sanda Za Su Sake Gudanar Da Babbar Zanga-Zanga A Gaban Majalisar Dokoki

Safiyatul Islam of Nigeria

Tijjaniya Youth Enlightenment Forum

Advertisement

Interfaith Parties for Peace and Development

Sairul Qalbi Foundation

Advertisement

Habbullah Mateen Foundation

Imams of Juma’at Mosques under Qadiriyya Movement

Advertisement

Committee of Sunnah Preachers, Kano

Multaqa Ahbab Alsufiyya

Advertisement

Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ya tabbatar da cewa takardun korafe-korafen sun mika zuwa Majalisar Shura domin ta yi cikakken nazari.

Korafe-korafen sun biyo bayan zanga-zangar da wasu kungiyoyin addini suka gudanar a Kano a jiya, inda suka nuna damuwa kan karatun Malam Lawan Triumph. Kungiyoyin sun ce malamin ya ketare hurumin wasu malamai, yayin da gwamna ya bukaci su kawo korafensu a rubuce domin daukar mataki.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending