Connect with us

News

‎Yadda Matar Wani Soja Ta Cinna Masa Wuta Ya Mutu ‎

Published

on

Unguwa gawa

Wani soja mai muƙamin Laftana a rundunar sojan Najeriya, Samson Haruna, ya mutu bayan da matarsa ta cinna masa wuta a lokacin da suka samu sabani a gida.

‎Lamarin mai cike da firgici da tausayawa ya faru ne a ranar 22 ga Satumba, 2025, a Wellington Bassey Barracks da ke Ibagwa, ƙaramar hukumar Abak, a jihar Akwa Ibom.

Ministan da PREMIUM TIMES ta bankado ya yaudari Najeriya da shaidun kammala karatu na Karya ya ajiye aiki

‎Rahotanni sun bayyana cewa matarsa, Mrs. Samson Haruna, ta watsa masa fetur sannan ta kunna masa ashana a lokacin da suke cikin zafafan maganganu a gida. Wannan ne ya haifar da mummunar ƙonewa a jikinsa gaba ɗaya.

‎Wata majiya ta tsaro ta shaida wa masani kan batutuwan tsaro a Najeriya, Zagazola Makama, wanda ya wallafa labarin a shafin sa na X (wanda ake kira Twitter a da), cewa marigayin wanda kuma likita ne a 6 Battalion Regimental Medical Office (RMO), an garzaya da shi asibiti bayan samun mummunar ƙonewa.

‎“An fara ba shi kulawar gaggawa a Military Reference Section (MRS) da ke cikin barikin, kafin daga bisani a tura shi zuwa University of Uyo Teaching Hospital don ƙarin jinya,” in ji majiyar.

‎Sai dai duk da ƙoƙarin da likitoci suka yi don ceto ransa, Laftana Haruna ya mutu sakamakon raunin ƙonewar da ya samu.

Advertisement

‎Hukumar tsaro ta tabbatar da cewa an kama matar, kuma tana hannun jami’an tsaro yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.

PLATINUM POST NEWS

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending