Connect with us

News

Fashewar Tankar Man Fetur Ta Hallaka Akalla Mutum 30 A Neja

Published

on

tanker fire

Mutane akalla 30 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu 40 suka jikkata a sakamakon fashewar wata tankar mai ɗauke da fetur a kan hanyar Agaie–Baddegi da ke jihar Neja.

Lamarin ya faru ne a kusa da kauyen Essa, dab da Agaie, da misalin ƙarfe 11 na safiyar Talata, kamar yadda mazauna yankin suka shaida wa LEADSHIP HAUSA

Advertisement

Gwamnatin Katsina Ta Fara Rushe Shagunan Da Aka Gina Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Wani mazaunin garin da ya ga yadda abin ya faru ya ce, “Tankar man ta yi hatsari ne tana sauka daga kan tudu, ta bugu da wata mota, nan take ta zube man fetur. Wasu matasa suka ruga domin kwaso man, sai kawai abin ya kama da wuta.”

Shaidu sun ce wutar ta bazu da sauri, inda ta kama motocin dake kusa da wajen, tare da kone mutane da yawa da ke kusa.

Advertisement

Shugaban Ƙungiyar Direbobin Tankar Mai ta Jihar Neja (PTD), Kwamared Farouk Mohammed Kawo, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa hukumomin kashe gobara da jami’an tsaro sun isa wurin domin taimakawa wajen kashe wutar da kuma ceto mutane.

Kwamared Kawo ya ce, “Lamarin abin takaici ne sosai. Da yawa daga cikin waɗanda suka mutu ba direbobi ba ne, amma jama’ar gari da suka yi gaggawar zuwa wajen don su kwaso man fetur.”

Advertisement

A halin da ake ciki, hukumomi sun rufe hanyar Agaie–Baddegi na ɗan lokaci, yayin da ake ci gaba da bincike kan ainihin musabbabin hatsarin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending