Connect with us

News

Gwamnatin Katsina Ta Fara Rushe Shagunan Da Aka Gina Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Published

on

FB IMG 1761045654324

Gwamnatin Jihar Katsina ta fara rushe shagunan jama’a da aka gina a gefen tituna da kuma kusa da gine-ginen gwamnati ba bisa ƙa’ida ba a cikin birnin Katsina.

Hukumar Tsara Birane da Gundumomi ta jihar (URPB) ce ke gudanar da aikin, da nufin tabbatar da bin ƙa’idojin gine-gine da kare muhalli da lafiyar jama’a.

Wasu ‘yan daba sun banka wa hedikwatar ADC a Ekiti wuta

Wuraren da aka fara da su sun haɗa da shatatalen High Court zuwa hanyar Daura, titun Sarki Abdulrahman, da kwaran High Court, tare da wasu muhimman sassan cikin birnin Katsina.

Wasu daga cikin masu shagunan da aka rusa sun bayyana rashin jin daɗi, inda suka zargi hukumomin da rashin bayar da isasshen lokaci ko damar gyarawa kafin rushe shagunan nasu.

Sai dai hukumar URPB ta ce aikin ba zai tsaya ba, har sai an share duk wuraren da aka gina ba bisa ƙa’ida ba, domin inganta kyawun birnin da tabbatar da tsaro da tsaftar muhalli.

 

Advertisement

 

KATSINA POST 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending