News
Wasu ‘yan daba sun banka wa hedikwatar ADC a Ekiti wuta
Wasu da ake zargin ‘yan daba ne sun cinna wuta ga sakatariyar jam’iyyar ADC da ke Ado-Ekiti, babban birnin jihar Ekiti, a daidai lokacin da ake shirin kaddamar da sabbin shugabannin jam’iyyar a jihar.
Wutar ta lalata kadarori da dama ciki har da tantin da ke daukar mutum 1000 da kujerunsa, da kuma wani bangare na ginin sakatariyar da aka banka wa wuta.
Mambobin jam’iyyar ADC sun yi Allah-wadai da harin, suna kuma kira ga hukumomin tsaro da su binciko wadanda suka aikata wannan ta’asa tare da gurfanar da su a gaban doka.
A halin yanzu, magoya bayan jam’iyyar sun taru a hanyar Basiri inda sakatariyar ta ke, suna jiran zuwan jagororin jam’iyyar na kasa da za su kaddamar da sabbin shugabannin.
-
News1 day ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News17 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
