Connect with us

News

An Tsinci Gawar Tsohuwa Mai Shekara 96 A Ramin Bayan-gida Bayan Kwanaki Huɗu Da Ɓacewa A Kano

Published

on

Hukumomi a Najeriya sun tsaurara matakan tsaro da kuma sa ido sosai a birnin Kano,

Hukumar kashe gobara a jihar Kano sun tabbatar da mutuwar wata tsohuwa ‘yar shekara 96, Habiba Ado, bayan da ta faɗa cikin ramin bayan-gida a ƙauyen Sarai, ƙaramar hukumar Dawakin Kudu.

Mai magana da yawun hukumar, ACFO Saminu Yusuf Abdullahi, ya bayyana cewa sun samu saƙon neman agaji ne da misalin 9:27 na safiyar ranar Alhamis, 6 ga Nuwamba, 2025, daga wani mazaunin yankin, Usman Adamu.

Advertisement

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Jami’o’i, Polytechnic, NCE Na Tsawon Shekaru 7

A cewar sanarwar, tawagar ceto ta isa wurin cikin gaggawa bisa umarnin daraktan hukumar, Alhaji Sani Anas, amma ta tarar da tsohuwar ta rigaya ta rasu.

Iyalanta sun sheda wa jami’ai cewa an shafe kwanaki huɗu ana neman ta, sannan kuma tana fama da larurar tabin hankali.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending