News
An cafke ‘likitan bogi’, An Rufe Asibitin Da Yake Gudanarwa Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Enugu sun cafke wani mutum da ake zargin yin aikin likitanci ba bisa ƙa’ida ba, tare da rufe wani asibiti da yake gudanarwa a garin Obollo-Etiti, ƙaramar hukumar Udenu.
Mutumin mai suna Kenneth Mamah na gudanar da asibiti da ya sanya wa suna St. Joseph Memorial Hospital, ba tare da rajista, horo, ko izini daga hukumomin lafiya ba.
An Soke Tashin Jiragen Sama Fiye Da 2,000 A Amurka Yayin Da Harkokin Gwamnati Ke Ci Gaba Da Dagulewa
A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a ta ma’aikatar, Ugodu Avemaria, ta fitar ranar Lahadi, an bayyana cewa samamen ya biyo bayan rahotanni daga jama’a da bayanan sirri da suka tabbatar da zargin. Samamen an gudanar da shi ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Lafiya na Jihar Enugu, Dr. George Ugwu.
Binciken jami’ai ya nuna cewa, Ana gudanar da ayyukan tiyata a ɗakin da ake karɓar marasa lafiya, ba a ɗakin tiyata ba.
Wurin ba shi da tsafta, kuma babu kayan aiki da suka dace.
Babu ƙwararrun ma’aikata, kuma wanda ke gudanar da asibitin bai da lasisin likita.
Sanarwar ta ce: “Yana gudanar da ayyukan lafiya masu hatsari, ba tare da izini ko cancanta ba, yana jefa rayukan al’umma cikin haɗari.”
Ma’aikatar Lafiya ta jihar ta yi kira ga jama’a da su rika kai rahoto kan duk wani wurin kiwon lafiya da ba ya bin ƙa’ida domin kare lafiya da rayuwar al’umma.
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News1 day ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News15 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
