Connect with us

News

Kotun Bangladesh Ta Yanke Wa Tsohuwar Firaminista Sheikh Hasina Hukuncin Kisa

Published

on

8b5309834c557ce7f41da711bb5988cb95144473040dbe8e4420e0827558352e

Wata kotu a Bangladesh a ranar Litinin ta yanke wa tsohuwar Firaminista Sheikh Hasina hukuncin kisa kan laifukan cin zarafin bil’adama, inda aka yi ta murna a cikin kotun da a yayin da alƙali ke karanto hukuncin.

An bayyana cewa Hasina, mai shekaru 78, ta ƙi bin umarnin kotu da ke buƙatar ta dawo daga Indiya domin ta halarci shari’arta kan zargin cewa ta umarci amfani da ƙarfi wurin daƙile zanga-zangar ɗalibai wadda ta kai ga kifar da gwamnatin ta.

Advertisement

Gobara Ta Yi Ajalin Yara Biyu ’Yan Gida Ɗaya

Wannan hukunci da jama’a suka dade suna jira, wanda aka watsa kai tsaye a talabijin na ƙasa, ya zo ne kafin zaɓen farko tun bayan kifar da ita a watan Agustan 2024.

“Duk wasu shika-shikan aikata laifuka kan bil’adama sun cika,” in ji alkalin kotun, Golam Mortuza Mozumder, yayin da yake karanta hukuncin ga kotun da ta cika makil a Dhaka.

Advertisement

An bayyana cewa an same ta “da laifi a tuhuma uku,” ciki har da hura wutar tashin hankali, bayar da umarnin kashe mutane, da kuma rashin ɗaukar mataki don hana aikata munanan abubuwan da aka aikata, in ji Mozumder

“Mun yanke shawarar yanke mata hukunci guda ɗaya — wato hukuncin kisa.”

Advertisement

 

TRT AFRIKA 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending