Connect with us

News

‎Gwamnatin Birtaniya Ta Yi Watsi Da Bukatar Dawo Da Ekweremadu Nijeriya Domin Ya Kammala Zaman Gidan Yari 

Published

on

129091850 ike ekweremadu 1

Gwamnatin Birtaniya (UK) ta yi watsi da bukatar gwamnatin tarayya na dawo da tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike Ekweremadu Nijeriya domin ya kammala tsawon shekarun da aka yanke masa na zaman gidan yari.

‎A halin yanzu, Ekweremadu yana zaman gidan yari a Birtaniya saboda hada baki wajen cire kodar wani matashi.

Advertisement

‎One Kano Agenda Ta Jinjinawa Gwamna Abba Kan Kasafin Kudin 2026 Na Naira Tiriyan 1 Da Biliyan 368

‎An yanke masa hukunci a watan Maris na 2023, inda aka yanke masa hukuncin shekaru tara da watanni takwas.

‎A farkon watan Nuwamba, Shugaba Bola Tinubu ya aika da wata babbar tawaga zuwa Landan don tattauna shari’ar Ekweremadu da kuma yiwuwar ya ci gaba da zaman gidan yarinsa a Nijeriya.

Advertisement

‎Tawagar ta kunshi Yusuf Tuggar, ministan harkokin waje, da Lateef Fagbemi, babban lauyan tarayya (AGF) kuma ministan shari’a.

‎Duk da haka, jaridar UK Guardian, wacce ta ambato wani jami’in ma’aikatar shari’a (MoJ), ta ruwaito cewa, an yi watsi da bukatar gwamnatin Nijeriya.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

LEADSHIP

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending