News
Dakarun Soji Sun Ceto Mutane 7 Da Aka Sace A Kano
Rundunar Sojin Najeriya karkashin Operation MESA ta ce ta ceto mutane 7 da aka sace a kauyen Yankamaye Cikin Gari da ke karamar hukumar Tsanyawa a jihar Kano.
A cewar sanarwar da Capt. Babatunde Zubairu, Mataimakin Daraktan Harkokin Yada Labarai na Rundunar Soji (3 Brigade), harin ya faru ne a daren ranar 29 ga Nuwamba, da misalin karfe 11 na dare.
An Hallaka Mutane 4, An Jikkata 10 Yayin Gudanar Da Shagalin Bikin ‘Birthday’
Capt. Zubairu ya ce an samu kiran agaji cewa wasu ‘yan bindiga masu yawa sun kai hari kauyen, sun hallaka wata mata mai shekaru 60 tare da sace mutane 10.
“Rundunar soji tare da jami’an ‘yan sanda suka tura tawaga zuwa wajen, inda suka bi sawun ‘yan bindigar zuwa kauyen Rimaye,” in ji Capt. Zubairu.
Ya kara da cewa sojojin sun yi musayar wuta da maharan, inda suka samu nasarar ceto mutane 7 daga cikin wadanda aka sace, yayin da ‘yan bindigar suka tsere zuwa karamar hukumar Kankia a jihar Katsina.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
