News
Dakarun Soji Sun Ceto Mutane 7 Da Aka Sace A Kano
Rundunar Sojin Najeriya karkashin Operation MESA ta ce ta ceto mutane 7 da aka sace a kauyen Yankamaye Cikin Gari da ke karamar hukumar Tsanyawa a jihar Kano.
A cewar sanarwar da Capt. Babatunde Zubairu, Mataimakin Daraktan Harkokin Yada Labarai na Rundunar Soji (3 Brigade), harin ya faru ne a daren ranar 29 ga Nuwamba, da misalin karfe 11 na dare.
An Hallaka Mutane 4, An Jikkata 10 Yayin Gudanar Da Shagalin Bikin ‘Birthday’
Capt. Zubairu ya ce an samu kiran agaji cewa wasu ‘yan bindiga masu yawa sun kai hari kauyen, sun hallaka wata mata mai shekaru 60 tare da sace mutane 10.
“Rundunar soji tare da jami’an ‘yan sanda suka tura tawaga zuwa wajen, inda suka bi sawun ‘yan bindigar zuwa kauyen Rimaye,” in ji Capt. Zubairu.
Ya kara da cewa sojojin sun yi musayar wuta da maharan, inda suka samu nasarar ceto mutane 7 daga cikin wadanda aka sace, yayin da ‘yan bindigar suka tsere zuwa karamar hukumar Kankia a jihar Katsina.
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News1 day ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News13 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
