Connect with us

News

Kungiyar Bakin Bulo Network for Better Tomorrow Ta Bukaci Gwamnatin Kano Ta Sake Duba Dokar Hana Goyo

Published

on

IMG 20251203 WA0006
Spread the love

Kungiyar Bakin Bulo Network for Better Tomorrow ta yi kira ga Gwamnatin Jihar Kano da ta sake duba dokar hana goyo ga masu baburan Lifan da aka fara aiwatarwa a birnin.

A cikin wata sanarwa da shugabanta, Bilal Nasidi Mu’azu, ya fitar a ranar Laraba, kungiyar ta bayyana damuwarta kan illolin da dokar ka iya haifar wa al’umma, musamman iyaye mata da masu karamin karfi.

Shugaba Tinubu Ya Yi Wata ganawar Sirri Da Hafsoshin Tsaro

Bilal ya ce mutane da dama na amfani da baburan su wajen kai yara makaranta da gudanar da hidindimun rayuwa, don haka takurawa irin wannan na iya jefa su cikin ƙalubale.

Sanarwar ta kuma bukaci Rundunar ’Yan Sandan Kano da ta yi la’akari da koke-koken jama’a, ganin cewa dokar za ta shafi rayuwar mutane da dama, musamman mata da masu kula da kananan yara.

Advertisement

Kungiyar ta yi addu’ar Allah ya sauƙaƙa wa al’ummar Kano tare da ba da mafita ga kalubalen da ke tattare da wannan mataki.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *