Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Yi Wata ganawar Sirri Da Hafsoshin Tsaro

Published

on

Tinubu 486x340
Spread the love

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wata ganawar sirri a jiya talata da hafsoshin tsaron kasar nan a Fadar Shugaban Kasa dake Aso Rock .

Taron sirri, wani bangare ne na kokarin da Gwamnatin Tarayya ke yi na kara kaimi wajen magance matsalar rashin tsaro da ke kara kamari a fadin kasar.

Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Ranar Fara Hutun Makarantun Firamare Da Sakandare

Hafsoshin tsaron sun isa Fadar da misalin karfe biyar na yamma, inda taron ya dauki kusan sa’o’i biyu.

Da yake magana jim kadan bayan kammala taron, Babban Hafsan Tsaro Janar Olufemi Oluyede, ya ce Shugaba Tinubu ya bayar da umarni tare da neman su matsa kaimi a yaki da matsalar rashin tsaro a kasar nan.

Advertisement

Janar Olufemi Oluyede ya bayyana taron a matsayin mai muhinmanci kuma ya nuna cewa ana sa ran sabon umarnin Shugaban kasar zai haifar da karin nasarori a ayyukan tsaro a kasar nan.

Taron ya zo ne sa’oi kadan bayan Shugaba Tinubu ya zabi tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), a matsayin Ministan Tsaro, bayan murabus din wanda ya gabace shi, Muhammad Badaru Abubakar ranar litinin, mako guda bayan an ayyana dokar ta-baci a kan matsalar tsaro.

 

TRUST RADIO LIVE

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *