Connect with us

News

‎Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Kubutar Da Ɗalibai 100 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Naje ‎

Published

on

nigeria school catholic 750x430

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa an kubutar da wasu dalibai 100 daga cikin ɗaliban da ’yan bindiga suka sace a makarantar St. Mary’s Private Catholic Primary and Secondary School da ke kauyen Papiri, a Karamar Hukumar Agwara ta Jihar Neja.

‎Hare-haren dai sun faru ne a ranar 21 ga Nuwamba, 2025, lokacin da ’yan bindiga suka isa makarantar da misalin karfe 2 na dare a kan babura, suka shiga dakunan kwanan dalibai na tsawon sa’o’i uku, inda suka tafi da mutane 315—dalibai 303 da malamai 12.

Ministan Tsaro Matawalle: ‘Yan Arewa, Dole Sai Mun Daina Yiwa Juna Hassada Sannan Allah Zai Tausaya Muna

‎Rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaro tare da mafarauta na yankin sun shiga dazuka da ɗakunan ɓoye domin bin diddigin masu garkuwa bayan harin.

‎A rana ta farko da faruwar lamarin, yara 50 sun yi nasarar tserewa, suka kuma haɗu da iyalansu. Sai dai mutum 265—ciki har da yara 253 da malamai 12—sun ci gaba da kasancewa a hannun ’yan bindiga.

‎A ranar Asabar, hukumomin tsaro suka tabbatar da ceto dalibai 100, abin da ya kawo sauƙin fargaba ga iyalai, duk da cewa sauran ɗaliban da malamai har yanzu suna tsare.

‎Gwamnatin Tarayya ta ce tana ci gaba da aiki tare da jami’an tsaro da gwamnatin Jihar Neja domin ganin an kubutar da sauran mutanen da ke hannun ’yan bindiga.

Advertisement

‎DAILY POST

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending