News
Gwamnatin Tarayya Da ASUU Za Su Kaddamar Da Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Ilimi A Najeriya
Gwamnatin Tarayya da Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) sun shirya bayyana wata gagarumar yarjejeniya da aka kulla domin karfafa zaman lafiya da inganta karatu a jami’o’in kasar nan jibi Laraba.
Mai magana da yawun ma’aikatar ilimi, Folasade Boriowo, ta ce za a gudanar da taron kaddamar da wannan yarjejeniya ne a babban dakin taro na hukumar TETFund da ke Abuja, karkashin jagorancin Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, da kuma Minista a ma’aikatar Ilimi, Farfesa Suwaiba Sa’id Ahmad.
Rikicin Manoma da Makiyaya Ya Yi Ajalin Mutane 10, Ciki Har da Kansila A Taraba
A cewar Madam Folasade, wannan yarjejeniya wani muhimmin mataki ne na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin inganta yanayin koyarwa da koyo da kuma sanya jami’o’in Najeriya su zama masu gogayya da sauran jami’o’in duniya.
Gwamnati ta jaddada cewa wannan mataki zai kara dawo da kwarin gwiwa ga dalibai da ma’aikata, tare da tabbatar da cewa an samu dorewar sauye-sauyen da za su samar da ingantaccen ilimi mai amfani ga daukacin ‘yan Najeriya
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
