News
Zazzabin Lassa Ya Yi Ajalin Mutum 17 A Jihohi 8 — Hukumar NCDC
Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa NCDC ta bayyana cewa a cikin makonni uku na shekarar 2026 zazzabin lassa ta yi ajalin mutum 17 a jihohi 8 a kasar nan.
Bisa ga sanarwan mako-mako da hukumar ke fitarwa a shafinta na yanar gizo ya nuna cewa a mako na uku na yaduwar cutar jihohin Bauchi, Taraba, Filato, Ondo, Edo, Ebonyi, Benuwe da Nasarawa sun samu kashi 46% a yaduwar cutar.
Hukumar ta ce daga wadannan jihohi an samu mutum 93 da aka tabbatar sun kamu da cutar.
Zuwa yanzu yaduwar cutar a 2026 ya kai kashi 18.1% Kasa da kashi 18.2% din da aka samu a 2025 a irin wannan lokaci.
NCDC ta ce jami’an lafiya hudu sun kamu da cutar a cikin mako na uku na yaduwar cutar.
Hukumar ta ce kashi 89% na mutanen da suka kamu da cutar an gano su ne daga jihohin Bauchi, Ondo, Taraba da Edo.
Matasa masu shekaru 21 zuwa 30 na daga cikin rukunin mutanen da suka fi kamuwa da cutar sannan maza sun fi mata kamuwa da cutar.
Har ya zu dai rashin sani, rashin zuwa asibiti da rashin tsaftace muhalli na daga cikin matsalolin dake ci gaba da yada cutar.
Gwamnati ta ce za ta ci gaba da kokari musamman ta hanyar daukan matakan da suka fi dacewa domin dakile yaduwar cutar.
