News
Gwamna Abba Ya Sauke Kwamishinan Kasuwanci Shehu Wada Sagagi
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da sauke Alhaji Shehu Wada Sagagi daga mukaminsa na Kwamishinan Ma’aikatar Zuba Jari, Kasuwanci da Masana’antu da nan take.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu.
Tirela Ta Murƙushe Matukin Babur
Wannan mataki ya fara aiki nan take.
Gwamnan ya umarci Alhaji Sagagi da ya mika ragamar ma’aikatar ga Babban Sakataren ma’aikatar.
Ana sa ran zai kammala mika ragamar aiki zuwa gobe da safe.
Gwamna Yusuf ya gode masa bisa gudunmawar da ya bayar a lokacin da yake rike da mukamin.
-
News5 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News4 days ago
ICPC Ta Wanke Femi Gbajabiamila Daga Zargin Badakalar Hukumar Bogi
-
News5 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Jariri Da Wasu Ma’aikatan Asibiti A Jigawa
