News
Mahara sun kai sabon hari a kauyen da suka kashe masu bikin aure a Kaduna
Rahotanni daga Jihar Kaduna na cewa ’yan bindiga sun kaddamar da sabon hari a kauyen Kahir da ke Karamar Hukumar Kagarko, inda suke harbi kan mai uwa da wabi.
Kawo yanzu dai babu wani karin bayani game da harin ko halin da mutane suke ciki bayan harin na ranar Talata.
Jama’a Sun Hallaka Barawon Waya A Kano
Wannan harin na zuwa ne bayan a ranar Lahadi da dare, ’yan bindiga sun bude wa mahalarta bikin aure wuta a kauyen, inda suka kashe akalla mutum 12, tare da yin garkuwa da wasu da dama.
Aminiya ta ruwaito cewa maharan sun kuma jikkata mutane da dama, inda aka garzaya da su Babban Asibitin Kagarko, wasu mutum biyu da ke cikin mawuyacin hali kuma aka wuce da su Kaduna domin kula da lafiyarsu.
Hukumar ’yan sanda ta tabbatar da harin na baya, ba tar da bayar da alkaluman wadanda abin ya shafa ba.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
