News
Jami’an NDLEA Sun Kama Mutane 21 Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) a Jihar Kano ta sanar da kama mutane 21 tare da kwace nau’ikan miyagun ƙwayoyi da makamai na gida, sakamakon samamen da ta gudanar a wasu yankunan jihar.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar a Kano, Sadiq Muhammad Maigatari, ya fitar, ya ce an gudanar da samamen ne a ranar 11 ga watan Afrilu, 2026, a wurare da dama da ake zargi da zama cibiyoyin safarar miyagun ƙwayoyi.
Fiye Da Mutane 1,100 Aka Sace A Arewacin Najeriya Cikin Watanni 4 – Amnesty
Wuraren da aka kai samamen sun haɗa da Filin Idi, Hotoro, Mariri, Fagge da kuma yankin Farm Center da ke kan titin Zariya.
Hukumar ta ce a yayin aikin, jami’anta sun samu nasarar cafke mutum 21 tare da ƙwato abubuwa daban-daban, ciki har da tabar wiwi, ƙwayoyin pregabalin, magungunan tari masu ɗauke da sinadarin codeine da kuma sinadarin roba da ake shaƙa domin maye. Haka kuma, an kwace wasu makamai na gida daga hannun waɗanda ake zargi.
Sanarwar ta ƙara da cewa wasu daga cikin waɗanda aka kama sun yi yunƙurin tserewa ko kai hari ga jami’an tsaro, amma jami’an sun yi amfani da dabaru wajen shawo kan lamarin tare da cafke su.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
