Connect with us

News

An Kashe Ministan Tsaron Mali A Harin Ta’addanci

Published

on

10941180 1777200075

Rahotanni daga Al Jazeera sun bayyana cewa an kashe Ministan Tsaron ƙasar Mali, Sadio Camara, a wani hari da ake zargin ‘yan ta’adda ne suka kai a ranar Lahadi.

Majiyoyin labarai sun ce maharan sun kai farmaki gidan ministan da ke garin Kato, wanda ke kimanin kilomita 15 arewacin Bamako, babban birnin ƙasar.

Advertisement

An Kashe Ministan Tsaron Mali A Harin ‘Yan Ta’adda

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a fitar da cikakken bayani kan yadda harin ya faru ba, yayin da hukumomin tsaro ba su yi cikakken bayani kan lamarin ba. Sai dai wannan harin na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar Mali ke fuskantar ƙalubalen tsaro daga kungiyoyin ‘yan ta’adda a sassa daban-daban na ƙasar.

Advertisement

Ana sa ran gwamnati za ta fitar da ƙarin bayani kan wannan lamari a nan gaba, yayin da jama’a ke ci gaba da nuna damuwa kan yadda hare-haren ta’addanci ke ƙaruwa a ƙasar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending