Connect with us

News

Dakarun Sojin Sama Sun Lalata Maboyar ‘Yan Bindiga A Katsina

Published

on

Wani Jirgin Rundunar Sojin Saman Najeriya Ya Hallaka Mutane Da Dama A Sokoto 

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta kai wani samame mai ƙarfi a jihar Katsina, inda ta lalata wata muhimmiyar maboyar ‘yan bindiga tare da kashe wasu daga cikinsu a dajin Dan-Aji da ke ƙaramar hukumar Faskari.

Harin, wanda aka kai ranar 1 ga watan Mayu, 2026, ya gudana ne karkashin rundunar Operation FANSAN YAMMA Sashi na 2, bayan samun sahihan bayanan sirri da suka nuna cewa ‘yan bindiga sun sake fara taruwa da ƙarfafa ayyukansu a yankin.

Advertisement

Dakarun Sojin Sama Sun Lalata Maboyar ‘Yan Bindiga A Katsina

A cewar jami’an tsaro, maboyar na da alaƙa da wani jagoran ‘yan bindiga mai suna Abasu Aiki, wanda ake zargi da jagorantar hare-hare a yankunan Faskari da Kankara da kuma Funtua.

Advertisement

Rahotanni sun nuna cewa jiragen rundunar sun gano ‘yan bindiga dauke da makamai suna zirga-zirga a kan babura a cikin dajin, kafin su kai wani daidaitaccen hari da ya hallaka wasu daga cikinsu tare da lalata gine-ginen da suke amfani da su.

Binciken bayan harin ya tabbatar da cewa an kashe mayaƙa da dama, yayin da aka rusa cibiyar ajiyar kayayyaki da sauran gine-ginen da ke taimaka musu. Haka kuma, harin ya haddasa gobara da fashewar abubuwa, alamar cewa an adana makamai da kayan aiki a wurin.

Advertisement

Jami’an rundunar sun bayyana cewa wannan farmaki ya taimaka matuƙa wajen dakile motsi da hanyoyin samun kayayyaki na ‘yan bindiga a yankin. Sun ƙara da cewa rundunar za ta ci gaba da kai irin waɗannan hare-hare domin rage ƙarfin ‘yan bindiga da dawo da zaman lafiya a Arewa maso Yamma.

Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da kokarin kawar da matsalar tsaro a yankunan Arewa maso Yamma na Najeriya.

Advertisement

 

PRNigeria

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending