Connect with us

News

‘Yan bindiga sun hallaka ‘yan sanda biyar da farar-hula 12 a jihar Katsina

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

 

 

 

Wasu ‘yan bindiga sun hallaka ‘yan sanda 5 da wasu farar hula akalla 3 a yankin karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina a Najeriya.

Advertisement

 

Bayanai sun nuna cewa yanzu haka ana can cikin wani yanayi na alhini a yankin karamar hukumar bayan harin da ‘yan bindigar suka kai a yammacin jiya Laraba.

Zargin kalaman ɓatanci: A canja alƙalin da ke yin shari’a ta — Abduljabbar

Kamar yadda wani mutumin yankin mai suna Shamsuddini, wanda ya rasa kawunsa a harin ya shaida wa BBC.

 

Haka kuma wasu rahotanni daga yankin karamar hukumar Faskari a jihar ta Katsina na cewa wasu hare-haren da ‘yan bindiga suka kai sun yi sanadin asarar rayuka akalla 9 cikin kwana biyu.

Advertisement

 

Shugaban karamar hukumar ta Faskari, Musa Ado Faskari, ya koka kan yadda hare-haren ‘yan bindigar ke dada munana a yankin nasa a ‘yan kwanakin nan.

 

Yayin da BBC ta tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan a jihar Katsinar, SP Gambo Isa, ya tabbatar da labarin harin da aka kai yankin na Kankara.

 

Kakakin ya jaddada cewa, rundunarsu tare da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro suna yin iya bakin kokari, don ganin sun murkushe wannan matsala ta tsaro a sassan jihar ta Katsina.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending