Connect with us

News

Hatsarin Mota: Mutum 30 Sun Kone Kurmus A Hanyar Zariya Zuwa Kano

Published

on

 

DAGA KHADIJA ABDULLAHI MAHMUD 

 

 

 

Akalla mutum 30 sun kone kurmus yayin da wasu fasinjoji 12 kuma suka sami raunuka a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a Tashar Musa da ke kan hanyar Zariya zuwa Kano a ranar Alhamis.

Advertisement

Da yake tabbatar da aukuwar hatsarin, Kwamandan Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) shiyyar Zariya, Abdulhamid Yakasai, ya ce motoci guda uku; kirar Homa guda biyu da Golf guda daya hatsarin ya shafa.

Zargin kalaman ɓatanci: A canja alƙalin da ke yin shari’a ta — Abduljabbar

Ya alakanta hatsarin da gudun wuce kima da kuma kokarin wuce na gaba ba tare da la’akari a da wasu direbobi ke yi ba a lokacin da suke tuki.

Yakasai ya kuma ce suna kokarin gano daga inda motocin suka taso da kuma lambobinsu domin sanar da ‘yan uwansu.

Tuni dai aka kai wadanda suka sami raunuka Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello (ABUTH) da ke Zariya tare da gawarwakin guda 30.

 

Advertisement

 

DAILY TRUST

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending